IQNA

UNESCO Ta Nuna Goyon Bayanta Ga Quds

22:39 - November 22, 2019
Lambar Labari: 3484265
Bangaren kasa da kasa, hukumar kula da harkokin al’adu ta duniya ta nuna goyon bayanta ga Quds

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, hukumar kula da harokin ilimi da al’adu ta duniya UNESCO ta nuna cikakken goyon bayanta kan kare wuraren tarihi na Quds na falastinawa.

Bayanin ya ce wannan taro da UNESCO ta gudanar ya samu halartar ministocin ula da harkokin al’adu na kasashe 120 naduniya wadanda dukkaninsu sun nuna goyon bayansu ga wannan mataki.

Bisa ga bayanin da ministocin suka fitar sun jaddada cewa, birnin Quds na falastinawa ne kamar yadda yake a cikin kudirin majalisar dinkin duniya.

A cikin shekara ta 1981 majalisar dinkin duniya ta saka tsohon  birnin quds da ke gabashin birnin a yanzu a cikin wuraren tarihi na duniya, amma a cikin 1982  majalisar ta bayyana yankin da cewa yana cikin hadari.

 

3858567

 

 

 

 

 

 

captcha