IQNA

Zaman Ministocin Kiwon Lafiya Na Kasashen Musulmi A Kasar UAE

20:05 - December 13, 2019
Lambar Labari: 3484316
Bangaren kasa da kasa, UAE za ta dauki nauyin taron ministocin kiwon lafiya na kasashen musulmi.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, shafin oic-oci.org ya bayar da rahoton cewa, kasar hadaddiyar daular larabawa za ta dauki nauyin taron ministocin kiwon lafiya na kasashen karo na bakawai, wanda zai duba ayyukan da aka yi da kuma wadanda za a yi takanin 2014 zuwa 2023.

Daga cikin muhimamn abubuwa da zaman taron zai yi dubi a kansu, akwai batun samar da allurer rigakafi ta kananna yara, wadda za a rika gudanarwa a karkashin kungiyara  cikin kasashen musumi.

Da kuma wasu batutuwa da suka shafi kiwon lafiya da suke a matsayin kalu bale ga kasashen musulmi, musamman marassa karfi daga cikinsu, da kuma yadda za a tallatafa musu a wannan fage.

3863738

 

https://iqna.ir/fa/news/3863738

captcha