Mista Diab, zai maye gurbin Saad Hariri, wanda ya yi murabus daga mukamin sakamakon zanga zangar data mamaye kasar.
Sabon firaminsitan Hassan Diab, na samun goyan bayan kungiyar Hezbollah ta kasar.
Shi dai Hassan ba sananne sosai ba a idon al’ummar kasar, amma ya taba rike mukamin ministan ilimi a shekara 2011.
Tun a cikin watan Oktoba ne kasar ta Labanon ke fama da jerin zanga zanga na al’ummar kasar dake kin jinin mahukuntan kasar da suke zargi da cin hanci da rashawa.
https://iqna.ir/fa/news/3865314