Kamfanin dillancin labaran IQNA, gwamnatin Siriya ta sanar da murkushe wani harin makamai masu linzami da mahukuntan yahudawa mamaya na Isra’ila suka kaddamar a cikin daren jiya a wasu sassan kasar.
Kamfanin dilancin labaren kasar, ya rawaito cewa makamman garkuwa kan hare haren sama sun murkushe wasu jerin hare haren makiya a kusa da Damascus babban birnin kasar.
Hare haren an kai su ne kan yankunan al-Kiswah da Marj al-Sultane da Jisr Bagdad, inda wuta kama a daya daga cikin sansanonin sojin gwamnatin Siriyar.
Wannan dai ba shi karon farko ba da Isra’ila da ke kai ire iren wadannan hare hare a Siriya ba, tun bayan barkewar rikicin kasar a cikin shekara ta dubu biyu da sha daya.