IQNA

Ayatollah Sistani Ya Yi Kira Da A Kare Rayuka Masu Neman Gyara

23:56 - February 07, 2020
Lambar Labari: 3484495
Babban malamin addini na kasar Iraki ya kirayi jami’an tsaron da su bayar da kariya ga masu zanga-zangar lumana.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, kamfanin dillancin labaran Saumaria News ya bayar da rahoton cewa, a cikin hudubar sallar Juma’a ta yau a na karanta sakon Ayatollaj Sistani.

Bayanin ya ce, Ayatollah Sistani ya jaddada a kan batutuwa biyu, na daya  daga cikinsu shi ne jama’a masu neman gyara da su yi amfani da hanyoyi na lumana, ba na tashin hankali ba.

Haka nan kuma ya kirayi jami’an tsaro da su kare masu zanga-zangar lumana domin neman a yi gyara a cikin harkokin tafiyar mulkin kasar.

Baya ga haka kuma ya kirayi gwamnati da ta gaggauta aiwatar da sauye-sauye domin al’ummar kasar ta gani a kasa, kamar yadda ya yi kira da a gudanar da zaben gaggawa.

 

https://iqna.ir/fa/news/3877123

 

 

captcha