Shafin yada labarai na sba۷egypt.com ya bayar rahoton cewa, Su’ad Abdulkadir tsohuwa ce mai shekaru 77 daga yankin Iskandariyya na kasar Masar, wadda da ta rubuta cikakken kwafin kur’ani mai tsarki.
Wannan mata tana ware sa'oi 7 zuwa 8 daga lokacin da ta yi sallar asuba, domin rubutun kur'ani mai tsarki, har zuwa lokacin da ta kammala wanda ya dauke ta shekaru biyu.
Daya daga cikin jikokinta ne dai ya dauki hotunanta kuma ya watsa a shafukan yanar gizo, inda ya bayyana cewa kakarsa ba ta yi karatu ba, amma Allah ya yi mata baiwar ta karatun kur'ani mai tsarki.