Shafin yada labarai na ajel.sa ya bayar da rahoton cewa, tun jiya ne aka fara gudanar da aikin feshin magani mai kashe kwayoyin cuta a cikin masallacin harami, inda aiki ya shafi bangaren dawafi, da hakan ya hada da bangaren hajarul aswad da ke jikin Ka’aba, sai kuma maqam Ibrahim (AS).
Abdulrahman bin Abdulaziz Al-sudais mai kula da haramin makka da masallacin manzon Allah (SAW) ya halarci wurin feshin, inda ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin kare lafiyar masu ziyara daga kamuwa da cutar corona mai hadari.