Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Musawi ya bayar da sanarwar cewa, Iran Muhammad Jawad Zarif ministan harkokin wajen kasar Iran, ya aike da wasika zuwa ga babban sakataren majalisar dinkin duniya kan wajabcin janye wa Iran takunkuman da wasu suka dora mata, domin yaki da corona.
Ya kara da cewa bayan haka kuma Zarif ya aike da wannan wasika zuwa ga wasu daga cikin ministocin harkokin waje na wasu kasashe, domin yi musu bayani kan muhimmancin sakon nasa.