Tashar Sky News ta bayar da rahoton cewa shugaban kasar Tunisia ya bukaci da a killace kasar saboda hana yaduwar cutar corona.
Shugaban na Tunisia a cikin wani jawabi da ya gabatar wanda aka watsa kai a gidajen talabijin, ya bayyana cewa dole ne a dauki matakan hana yaduar cutar a cikin kasar.
Ya ce dole n mutane su daina tafiye-tafiye kamar yadda jami’an kiwon lafiya suka bukata.
Yanzu haka dai Tunisia ta rufe masalatai da makarantu da kuma iyakokinta na sama da kasa da ruwa, kuma mutane 54 ne suka kamu da cutar yanzu haka a kasar.