Tashar euro news ta bayar da rahoton cewa,a yau wani abu mai karfi ya tarwatse a cikin wata makaranta a yankin Takhar a kasar Afghanistan.
Rahoton ya cea n tabbatar da mutuwar mutane tara da kuma jikkatar shida, amma babu cikakken bayani kan hakikanin abin da ya faru.
Wasu bayanan sun ce wasu manyan harsasai ne a ka ajiye a cikin makarantar wadanda suka tarwatse, kuma suka kashe daliban ad suke a wurin.
Wasu bayanan kuma na cewa akwai yiwuwar an harba makamin roka ne wanda ya sauka a cikin makarantar, kuma ya tarwatsa wani bangaren gininta tare da kashe mutane.
A halin yanzu jami’an tsaro suna gudanar da bincike kan hakikanin abin da ya faru kafin dora alhakin hakan a kan wani bangare.