IQNA

Magoya Bayan Sheikh Zakzaky A Najeriya Sun Yi Tattaki

22:20 - October 07, 2020
Lambar Labari: 3485254
Tehran (IQNA) Mabiya Sheikh Zakzaky suna gudanar da tattakin arbaeen a wasu yankunan na Najeriya domin raya ranar arbain.

Mabiya mazhabar ahlul bait suna gudanar da tattakin arbain a cikin da wajen kasar Iraki domin raya ranar  ta arbaeen na shahadar limami na uku daga cikin limaman tsira na ahlul bait.

A Najeriya ma mabiya mazhabar Ahlul bait karkashin jagorancin Sheikh Zakzaky suna gudanar da irin wadannan taruka da tattaki, inda a yau a cikin jihar Kano an gudanar da irin wannan tattakin tare da halartar daruruwan jama’a, domin raya wannan rana ta arbaeen.

A daidai lokacin da ranar arbaeen ke karatowa, ana ci gaba da gudanar da tattaki a cikin kasar Iraki daga sassa daban-daban na kasar zuwa birnin Karbala mai alfarma, domin halartar tarukan arbaeen da aka saba gudanarwa a kowace shekara, inda za a gudanar tarukan na wannan shekara a ranar Alhamis mai zuwa.

Rahotanni sun ce miliyoyin mutane ne suke gudanar da tattakin a cikin kasar, duk kuwa da cewa a wannan shekara an dauki kwararan matakai na takaita yawan masu halartar taron, musamman daga kasashen ketare.

Mahukuntan kasar sun bayyana cewa sun dauki matakan ne domin dakile yaduwar ctar corona a tsakanin jama’a, inda hatta wadanda suka tafi wannan ziyara a cikin kasar, an lizimta musu wasu ka’idoji wadanda dole ne su kiyaye su, kamar saka takunkumin fuska, wanke hannu akai-akai, da kuma bayar da tazara.

 

3927817

 

 

captcha