A yau Laraba ne dai wani abu mai fashewa da aka dasa a makabartar da ba ta musulmi ba a birnin Jidda na Saudiyya, ya fashe inda ya yi wa wasu mutane da dama rauni.
Kakakin fadar gwamnatin gundumar Makka mai alfarma ya shaida wa manema labaru cewa; Jami’an tsaro sun fara gudanar da bincike akan harin da aka kai a yayin da karamin jakadan kasar Faransa ya halarci makabartar.
Sultan al-Dusary ya kara da cewa; Wani ma’aikacin karamin ofishin jakadancin Girka da wani jami’in tsaron Saudiyya sun jikkata.
A can birnin Paris kuwa, ma’aikatar harkokin wajen Faransa ce ta sanar da cewa; Nakiyar ta tashi ne a lokacin da ake gudanar da kwarya-kwaryar bikin tunawa da yarjejeniyar tsagaita wutar yakin duniya na farko a ranar 11 ga watan Nuwamba na dubu daya da dari tara da sha takwas.
3934713