Tashar CBC ta bayar da rahoton cewa, Justin Trudeau firayi ministan kasar Canada ya fitar da wani bayani na tunawa da musulmin da aka kashe a masallacin garin Quebec shekaru hudu da suka gabata.
A cikin bayanin nasa ya bayyana cewa, a kowace shekara ana fitar da bayani da kuma yin taro na tunawa da wadannan musulmi da aka yi wa kisan gilla a cikin masallaci, amma a wannan karon ya kudiri aniyar sanya wannan rana ta zama ranar tunawa da wadannan musulmi a hukumance a kasar Canada.
Ya ce sanya wannan rana ta zama ranar tunawa da su a hukumance yana hakan yana da matukar muhimamnci, domin kuwa hakan zai sanya wannan lamari na bakin ciki da takaici ya zama a raye a cikin zukatan dukkanin al’ummar Canada har abada.
Baya ga haka kuma sun cancanci hakan, domin kuwa an kashe sun ea cikin masallaci a lokacin da suke yin ibada ba tare da sun yi wa kowa laifi ba, kuma hakan zai sanya a ci gaba da kara kyamar irin wanann aiki na ta’addanci da zalunci da nuna kiyayya ga musulmi.
A ranar 29 ga watan Janairun 2017 ne wani matashi mai tsananin kiyayya da musulmi ya shiga masallacia Quebec ya budewa musulmi wuta alokacin da suke salla, ya kashe 6 ya kuma jikkata wasu.