Shafin yanar gizo na ofishin jagora ya bayar da bayanin cewa, jagoran juyin juya halin muslunci na kasar Iran ya yabawa 'yan wasan kwallon raga na kasar da suka lashe kofin zakarun nahiyar Asia.
A cikin matanin bayanin wanda ya zo kamar haka:
Da Sunan Allah Mai Girma
Nasarar da 'yan wasan kasar Iran suka samua wasannin cin kofin zakarun nahiyar Asia, babban abun murna ne da farin ciki ga daukacin al'ummar kasar.
Ina mika godiya ta musamman ga dukkanin matasa 'yan wasa da suka nuna kwazo, da kuma masu horar da su har su kai ga samun wannan nasara.
Sayyid Ali Khamenei
20 Satumba 2021