Kamfanin dillancin labaran kafil ya bayar da rahoton cewa, a jiya dubban mutane su taru a hubbaren Abbas da ke birnin Karbaka na Iraki, domin murnar maulidin manzon Allah (SAW).
A kowace shekara dubban musulmi suna taruwa a wannan hubbare domin murnar zagayowar lokacin maulidin manzon Allah (SAW).
Masu hidima a wannan hubbare ne dai suke raba furanni ga masu ziyara, ayyin da kuma malamai kan gabatar da jawabai kan matsayin ma'aiki, da kuma daukar darussa daga rayuwarsa mai albarka.