A rahoton da gidan rediyon Faransa ya bayar, ‘Yan bindigar sun kai harin ne a Asubahin wayewar garin jiya Alhamis.
Har ya zuwa lokacin hada rahoton ba a sami wani bayani ba daga Gwamnatin jihar Nejan ba, sai dai kwamishinan ‘Yan sandan Jihar Monday Bala Kuryas wadda ya tabbatar da kai hari ya ce Mutane 9 ne suka rasa rayukansu.
Wannan dai shine karo na 2 da ‘Yan bindigar suka kai irin wannan hari ga masu sallah a karamar hukumar Mashegun.
A kwanakin Baya ma ‘yan bindagar sun kashe Mutane 18 a dai dai lokacin da suke Sallar Asuban a garin Maza kuka dake yankin Mashegun.
4019874