Rahotanni sun ce, Jami'an 'yan sandan gwamnatin sahyoniyawan sun kutsa kai cikin masallacin Al-Aqsa daga Bab al-Magharbeh domin nuna goyon bayansu ga 'yan sahayoniyawan a safiyar yau ranar Talata 27 ga watan Disamba.
Dakarun ‘yan sandan yahudawan sahyoniya da sauran yahudawan sun yi maci a harabar masallacin Al-Aqsa inda suka gudanar da ibadar Talmud na Yahudawa a kusa da Bab al-Rahma da ke gabashin masallacin mai alfarma.
Yahudawan sahyoniyawan 'yan mamaya na ci gaba da kai hare-hare akai-akai a masallacin Al-Aqsa.
Bisa ga yadda dokokin kasa da kasa na majalisar dinkin duniya suka tanada, ofishin kula da bayar da agaji na birnin Quds da ma'aikatun kasar Jordan ne kawai a hukumance ke da hakkin bayar da izinin shiga wuraren ibadar musulmi idan har akwai bukatar hakan, amma yahudawa suna yin gaban kansu a duk lokacin da suka ga dama.