IQNA

Al-Shabab ta kashe mutane 8 a Somaliya

18:34 - January 12, 2022
Lambar Labari: 3486811
Tehran (IQNA) Mutane akalla 8 ne suka mutu sakamakon harin bam da aka kai da wata mota a kusa da filin sauka da tashin jiragen sama na Mogadishu babban birnin kasar Somaliya.

Tashar Russia Taoday ta bayar da rahoton cewa, karar fashewar bama-baman ta girgiza babban birnin kasar ta Somaliya a yau da rana tsaka, inda jama’a da dama suka kidime..

An dai kai harin ne a kusa da filin jirgin saman Mogadishu, a cewar majiyoyin gwamatin kasar.

Harin ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane takwas tare da jikkata wasu da dama.

Kungiyar ta'addanci ta al-Shabaab ta dauki alhakin kai harin kamar yadda ta saba yi, inda ta yi ikirarin cewa ta kai harin ne a kan wani ayarin motocin da ke dauke da wasu jami'ai farar fata.

Mohammad Abdi, jami'in tsaro a birnin Mogadishu, ya ce an samu barna a wurin da fashewar ta faru, yana mai nuni da yiwuwar karuwar asarar rayuka.

Kungiyar Al-Shabaab da ke ikirarin kusanci da al-Qaeda, tana fafatawa da gwamnatin tsakiyar Somaliya tun shekara ta 2008, inda daga lokaci zuwa lokaci kungiyar ta kai munanan hare-hare a Mogadishu da wasu sassan kasar, tare da kashe mutane masu tarin yawa.

 

4028151

 

 

 

 

captcha