IQNA

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sakamakon Rushewar Ginin Majami'a A Niger Delta Ya Yana Karuwa

16:51 - January 13, 2022
Lambar Labari: 3486815
Tehran (IQNA) Adadin mutanen da suka mutu a lokacin da wata majami'a mai hawa uku da ta ruguje a jihar Delta ta Najeriya yana karuwa, inda yanzu adadin ya kai mutane 10.

Kamfanin dillancin labarabn anatoli ya bayar da rahoton cewa, ya zuwa yanzu dai Akalla mutane 10 ne suka mutu sakamakon rugujewar gini mai hawa uku na coci a yankin Okpanam da ke Najeriya, kamar yadda kwamishinan lafiya na Najeriya Onunie Mordi ya bayyana a wata sanarwa.

Ya bayyana damuwarsa kan karuwar adadin wadanda suka mutu, yana mai cewa an ceto wasu mutane takwas kamar yadda rahotannin farko suka bayyana.

Ana ci gaba da aikin neman agaji da ceto a yankin, kuma ana jinyar wadanda suka jikkata a asibiti.

An ce sama da mutane 50 ne suka halarci cocin a lokacin da lamarin ya faru.

 

4028285

 

 

captcha