IQNA

Shirin Iran na kula da masu ziyarar Arbaeen su 400,000

14:53 - July 02, 2022
Lambar Labari: 3487496
Tehran (IQNA) Shugaban hedkwatar cibiyar Arbaeen Husaini (AS) ya sanar da cewa, an mika wa dakarun kare juyin juya halin Musulunci alhakin gudanar da aikin ziyarar Arbaeen daga waje nda ya ce: Ana sa ran masu ziyara 400,000 daga Iran za su shiga kasar Iraki a wannan shekara.

A wata hira da ya yi da IQNA, Sidmjid Mirahmadi, shugaban babban ofishin Arbaeen Hosseini (AS) ya bayyana dangane da masu ziyara daga  waje da suka shiga Iran za su  bar kasar zuwa zuwa Iraki domin ziyarar  Arbaeen, inda ya ce za su yi amfani da iyakokin Iran wajen  shiga da fita .

Ya sanar da shirye-shiryen kan iyakar Rimdan (iyakar da ke tsakanin Iran da Pakistan) don shiga da kuma fita kan iyakar Shalamcheh don fitar da masu ziyara daga kasashen Pakistan da sauransu ta iyakokin Iran zuwa Iraki.

Ya kara da cewa, a kowace shekara ana samun masu shigowa Iran domin zuwa Iraki daga kasashen  duniya daba-daban, da hakan ya hada da masu bi ta hanyar jiragen sama, da kuma masu bin hanyoyi na iyakar kasa.

4067740

 

 

captcha