IQNA

Labarai Kan Arbaeen:

An bayar da hutu a ranar Lahadi a hukuamnce a kasar Iraki saboda Tarukan Arbaeen

13:44 - September 14, 2022
Lambar Labari: 3487852
Hukumomin kasar Iraki sun sanar da cewa, yanzu haka dai miliyoyin mutane ne daga ciki da wajen kasar suka isa birnin Karbala da ke kudancin kasar domin halartar tarukan ziyarar arbaeen na Imam Hussain (AS).

Firayi ministan kasar Iraki Mustafa Alkazimi ya sanar da cewa, an dauki dukkanin matakan da suka dace domin tabbatar da cewa tarukan sun gudana lami lafiya, tare da sanar da cewa ranar Lahadi mai zuwa za ta kasance ranar hutu a hukumance, kasantuwar tarukan na Arbaeen za su kasance ne a ranar Asabar.

Gwamnan Lardin karbala ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu miliyoyin mutane suka iso birnin domin halartar wadannan taruka, kuma an dauki dukkanin matakan da suka dace na daukar bakuncin masu ziyara, da hakan ya hada da daukar kwararan matakan tsaro, samar da ababe bukatar rayuwa, da kuma tanadin kayayyakin ayyuka a bangaren lafiya.

A ranar Asabar mai zuwa ce za a gudanar da tarukan na arbaeen a birnin karbala, wanda ake sa ran mutane fiye da miliyan 20 za su halarta, daga ciki da wajen kasar Iraki.

4085425

 

 

captcha