IQNA

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Na Fatar Ganin Duniya Ba Tare Da Makaman Nukuli Ba

13:29 - March 04, 2009
Lambar Labari: 1751509
Bangaren siyasa: Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musulunci ta Iran Manochehr Mottaki, ya bayyana cewa babban burin Iran shi ne a wayi gari babu makaman kare dangi a duniya.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga bangaren yada labarai na ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran cew; a zaman da aka gudanar a birnin Geneva na kasar Szitzerland dangane da kawar da makaman kare dangi a duniya, ministan harkokin wajen kasar Iran Manochehr Mottaki ya bayyana cewa; babban burin Iran shi ne a wayi gari babu sauran makaman kare dangi a duniya, domin a cewarsa babbar barazana ga zaman lafiyar duniya ita makaman kare dangi, wanda kuma madamar wasu kasashe za su ci gaba da mallakar irin wadannan makamai, to kuwa duniya ba ta ga zaman lafiya ba.
Ya ce Iran ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya a duniya, kuma za ta ci gaba da yin riko da abin da ta rattaba hannu kansa.

372096
captcha