Bangaren kasa da kasa, za agudanar da wani tattaunawa mai taken musulunci a wannanzamani, daga nahiyar turai zuwa sauran kasashen msulmi, wanda zai samu halartar masana daga kasashen musulmi da na turai, inda za a gabatar da laccooci da makaloli dangane da muhimmancin samun fahimtar juna.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo an bayyana cewa, za agudanar da wani tattaunawa mai taken musulunci a wannanzamani, daga nahiyar turai zuwa sauran kasashen msulmi, wanda zai samu halartar masana daga kasashen musulmi da na turai, inda za a gabatar da laccooci da makaloli dangane da muhimmancin samun fahimtar juna tsakanin musulmi da sauran al’ummomi.
A wani labari da ya nakalto daga shafin sadrawa na yanar gizo na algeriesoir an bayyana cewa, an gudanar da sallar juma’a abirnin Rom fadar mulkin kasar Italia a babban dandalin da ke tsakiyar birnin, domin nuna rashin amincewa da matakin da mahukuntan suka dauka na kin bayar da izinin gina masallaci a birnin wanda ake kallaonsa amatsayin babban birnin na mabiya addinin kirista.
Bayanin ya ci gaba da cewa mabiya addnin muslunci na kasar Italia musamman ma mazauna birnin Rom, suna ganin cewa bisa la’akari da yawan da suke da shi a kasar, daidai da ddokokin da aka amince da su auna da ahakkin su mallaki babban masallacin juma’a a cikin birnin Roma, kuma sun aike da takardun neman izini kan hakan, amma har yanzu mahukunta ba su ce komai ba. 795365