Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar
gizo na QAF cewa, cibiyar Ruqayyah ta mabiya mazhabar shi’a na kasar saudiyyah
mazauna birnin Qom, sun shirya taro a makarantar Imam Mahdi (AJ) a yau, kan
mahangar Ahlul bait (AS) kan kur’ani.
Bayanin ya
ci gaba da cewa Sheikh Abdulmuhsen Aljuzairi daya daga cikin manyan malamai na
yankin Ihsa na kasar Saudiyya shi ne zai gabatar da jawabi a taron.
Cibiyar
sayyidah Ruqayyah (SA) tana bayar da muhimmanci matuka wajen shirya taruka da
suka danganci kur’ani mai tsarki ga daliban addini yan kasar ta Saudiyya da
suke zaune a birnin Qom, da hakan ya hada da koyar da ilmomin kur’ani da kuma
ilimin tajwidi.
Sheikh
Abduljalil Almakrani shi ne wandaya shirya tare da daukar nauyin gudanar da
wannan taro.