IQNA

Jami’an Diflomasiyya Da Dama Sun Watsi Da Gayyatar Bude Ofishin Jakadancin Amurka  

23:44 - May 13, 2018
Lambar Labari: 3482654
Bangaren kasa da kasa, fiye da jami’an diflomasiyyar kasashen turai 40 ne da suke sra’ila suka yi watsi da gayyatar bude ofishin jakadancin Amurka a Quds.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jami’an diflomasiyya fiye da 80 ne daga kasashen duniya aka gayyata domin halartar bikin bude ofishin jakadancin Amurka  a birnin Quds, amma da dama daga cikin sun ki karba gayyatar.

Daga cikin jakadun kasashen da aka gayyata mafi yawan jakadun kasashen turai ba za su halarci wurin ba, da suka hada har da jakadun Jamus, Birtaniya, Faransa da kuma Italia.

A gobe 14 ga watan Mayu ne za a bude ofishin jakadancin na Amuka, wanda aka gina a birnin Quds,a  matsayin amincewa da wannan birnin mai alfarma a matsayin fadar mulkin yahudawan Sahyuniya.

3713960

 

captcha