Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Mamdun Sise ya kasance daya daga cikin wadanda suka halarci gasar karatu da hardar kur’ani ta duniya ta daliban kasashen musulmi a jamhuriyar musulunci ta Iran.
Karamin jakadan Iran a Senegal Sayyid Hassan Esmati shi ne ya mika wadanann hotuna ga kamfanin dillancin labaran iqna, wadanda aka dauka alokacin kammala gasar.
Mamdun fitaccen makarancin kur’ani ne kuma mahardace wanda kuma dan darika ne da yake bin tafarkin sufanci na tsarkake zuciya.