IQNA

An Girmama Mahardata Kur’ani 135 A Kasar Masar

23:32 - April 02, 2019
Lambar Labari: 3483511
Bangaren kasa da kasa, an girmama wasu dalibai 135 dukkanin mahardata kur’ani a kasar Masar.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, an gudanar da taron girmama wasu dalibai 135 mahardata kur’ani a kasar Masar a lardin Bahrul Ahmar.

Rahoton ya c dukkanin wadannan maardata sun fito daga lardin an bahrul Ahmar inda mahukunta  ajahar suka dauki nauyin bayan da kyautuka na musamman a gare su.

Babbar manufar hakan dai ita ce karfafa dalibai da matasa kan lamarin kur’ani mai tsarki a fadin kasar ta Masar.

Haka nan kuma a daya bangaren an girmama iyaye mata abin koyi na shekara ta 2019, saboda tarbiyantar da yaransu kan kur’ani.

3800391

 

captcha