Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, tun a jiya ne aka baza jami’an tsaron yahudawa a kan dukkanin manyan titunan birnin Quds, musamman masu isa zuwa masallacin Aqsa mai alfarma.
Rahotoon ya ce da jijjifin safiyar yau an kara yawan jami’an tsaron yahudawa a ciki da wajen birnin Quds, inda suke daukar kwararan matakai a kan masu tafiya zuwa masallacin Aqsa domin sallar Juma’a.
Wannan mataki dai na zuwa ne da nufin hana gudanar da duk wani motsi da ked a alaka da ranar Quds ta duniya, inda bisa al’ada dubban daruruwan musulmi ne daga sassa daban-daban na Palestine suke halartar masalalcin Aqsa a wanann rana, inda bayan kammala sarra Juma’a, akan rera take da ke jaddada aniyar muuslmi da Falastinawa, kan cewa babu ja da baya dangane da batun Quds.
Ko a yau jami’an tsaron yahudawan sun kashe wani bafalastine dan shekaru 19 da haihuwa, bisa zargin cewa yana yunkurin kai musu farmaki da wuka.