Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a cikin wani sakon da ta aike a jiya, cibiyar azahar ta mika sakon ta’aziyya dangane da rasuwar daliban kur’ani sakamakon wata gobara a Liberia tare da rokon Allah yayi musu rahama.
A daren Talata da ta gabata ce dai wata gobara ta tashia cikin wata makarantar kur’ani a birnin manrovia fadar mulkin kasar Liberia, inda yara daliban kur’ani 27 tare da malamansu guda biyu suka rasa rayukansu.
Jami’an ‘yan sanda sun ce ba a san dalilin tashin gobarar ba, amma har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabinta.