Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga jaridar Daily Trust ta Najeriya cewa; Bello Muhammad Matawalle gwamnan jihar Zamafara ya bayyana cewa, ba za su daga kafa ga duk wanda yake ta alfarmar kur’ani mai tsarki a jiharsu ba.
Matawale yce an kafa kwamitin ne domin bin kadun lamarin tare da gno masu hannu a cikin lamarin, ya ce za a hukunta duk wanda aka samua cikin wanann lamari na keta alfarmar kur’ani ba tare da la’akari da matsayinsa ba ko shi wane ne.
A cikin makon da ya gabata ne dai aka keta alfarmar kur’ania wata makaranta a garin Gusau fadar mulkin jihar Zamafara, lamarin da ya daga hankulan al’ummar jihar.