IQNA

Daesh Ta Sake Dawowa A Cikin Tufafin Al’ummar Iraki

18:10 - November 28, 2019
Lambar Labari: 3484280
Mataimakin shugaban majalisar dokokin Iran kan harkokin kasa da kasa ya bayyana cewa daesh ta sake dawowa Iraki.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, Hussain Amir Abdollahian babban mataimakin shugaban majalisar dokokin kasar Iran kan harkokin kasa da kasa ya bayyana cewa; ‘yan ta’addan daesh sun sake dawowa amma a cikin fararen kaya na al’ummar Iraki.

Ya bayyana hakan ne a cikin shafinsa na twitter jim kadan bayan wani hari da aka kai kan karamin ofishin jakadancin Iran da ke birnin Najaf.

Ya e a fili yake kan cewa Amurka da Saudiya da kuma Isra’ila ne suke da hannu wajen daukar nauyin dukkanin abin da yake faruwa a Iraki na ta’addanci, amma a wannan karon ‘yan ta’addan da wadannan kasashen suke yin amfani da su sun sake bayyana ne amma a cikin farin kaya.

3860223

 

 

captcha