Shafin yada labarai na Almisriyun ya bayar da rahoton cewa, Abdultif Al Sheikh minsta mai kula da harkokin addini a kasar saudiyya ya sanar da cewa, saboda tsoron yaduwar cutar corona, an bayar da hutu a makarantun kur’ani na kasar.
Ya ce tun kafin wannan lokacin suna daukar matakan da suka dace domin tabbatar da cewa an kaucewa yaduwar cutar a tsakanin jama’a, wanda hakan ya hada taruka na mutane da yawa awuri guda.
Ya ce tsarin karatu na halka da ake yi a kasar inda mutane da dama suke taruwa a wuri guda yana da hadari, kuma za a iya kamuwa da cutar matukar aka yi rashin sa’a wani mai dauke da ita ya shiga wurin.
Yanzu haka dai cutar corona ta kama mutane kimanin dubu 109 a fadin duniya, inda ta yi sanadiyyar mutuwar fiye da 3,800 daga cikinsu.