Shafin yada labarai na Sanad lilanba ya bayar da rahoton cewa, kakakin kungiyar Hamas Sami Zuhri ya bayyana cewa, ci gaba da kakaba takunkumin Amurka a kan Iran, cin zarafin ‘yan adam ne.
Ya ce lokaci yay i da Amurka za ta janye takunkumanta na zalunci a kan Iran musamman a wannan lokaci da ake fama da cutar corona a kasar.
Wannan martani na Hamas ya zo ne domin nuna takaici kan yadda Amurka ta kara saka takunkumi a kan mutane 15 da kamfaoni 5 na kasar Iran.
Sabon takunkumin na Amurka ya hada da kamfanonin sufuri, kasuwanci, gine-gine, da kuma wani kamfanin makamashi.
A cikin wanann makon ne kasashe 8 suka aike da wata wasika zuwa ga babban sakataren majalisar dinkin duniya, da ke kiransa da ya dauki matakin tilasta wa Amurka jane takunkumanta akan kasar Iran cikin gaggawa.