Jaridar Al-nahar ta kasar Lebanon ta bayar da rahoton cewa, jiragen yakin kawancen Saudiyya sun kaddamar da hare-harea yau a kan yankuna daban-daban a cikin birnin San’a fadar mulkin kasar Yemen, da ma wasu biranen kasar ta Yemen.
Wannan rahoton ya ce wadannan hare-hare na zuwa ne a daidai lokacin da yakin Saudiyya kan kasar Yemen ya shiga shekara ta shida a jere, ba tare da masarautar Saudiyya ta iya mamaye kasar ta Yemen kamar yadda ta yi zato ba tun daga farko.
A daya bangaren kafofin yada labaran kasar Yemen sun bayar da rahotanni kan cewa, hare-haren na Saudiyya sun yi barna a birnin San’a da kuma biranen Alhudaidah, gami da Sa’adah da Maarib da sauransu
Sai kuma a nasu bangaren dakarun kasar ta Yemen sun sanar da cewa, wadannan hare-hare ba za su wuce ba tare da mayar da mummunan martani na daukar fansa ba kan abin ke faruwa.