IQNA

Martanin Iran Kan Take-Taken Amurka A Cikin Kasar Iraki

23:48 - April 01, 2020
Lambar Labari: 3484672
Tehran (IQNA) kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya mayar da martani dangane da take-taken Amurka  cikin kasar Iraki.

Sayyid Abbas Musawi kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran a lokacin da yake ya mayar da martani dangane da take-taken Amurka  cikin kasar Iraki ya bayyana cewa, abin da kasar Amurka take yi a halin yanzu a cikin Iraki ya sabawa dukkanin kiraye-kirayen da majalisar dinkin duniya da sauran bangarorin kasa da kasa suke yi, kan wajabcin nisantar duk wani tashin hankali a ko’ina cikin dunya, domin fuskantar corona.

Ya ce Amurka ba ta mutunta gwamnatin Iraki balantana al’ummarta, domin kuwa wakilan al’ummar Iraki a majalisar kasar sun kada kuri’ar da ke nemen ficewar Amurka daga kasar, amma tana ci gaba da yin biris da wannan kira.

3888532

 

Abubuwan Da Ya Shafa: Abbas Musawi biris amurka iraki take-taken
captcha