Kamfanin dillancin labaran Saumaria Nws ya bayar da rahoton cewa, ma’aikatar harkokin cikin gida ta kasar Saudiyya ta sanar da cewa, daga yau 2 ga watan Afirilu an kafa dokar hana fita da kai komo a cikin biranan Makka da Madina.
Sanarwar ta ce an dauki wannan mataki ne da nufin daikile yaduwar cutar corona a cikin kasar, kasantuwar wadannan birane biyu nan ne aka fi gudanar da harkoki wasu tara jama’a.
Wannan doka ta shafi ‘yan kasa da ma baki ‘yan kasashen ketare da suke a cikin kasar a halin yanzu, duk da cewa akwai ma’aikata a wasu bangarori da dokar ba ta shafe su ba, kamar jami’an tsaro, da ma’akatan kiwon lafiya da sauransu.
Tun a cikin makon da ya gabata ne dai sarkin masarautar Saudiyya ya bayar da umarnin daukar kwararan matakai na dakile yaduwar corona a kasar, musamman a biranan Riyad, Makka da kuma Madina.