Tashar talabijin din al-Masirah ta kasar Yemen, ta ambato majiyar tsaron kasar tana cewa Harin da jiragen yakin kawancen Saudiyya su ka kai a yankin Abas, da ke gundumar Hajjah, ya yi sanadin shahadar mutane hudu daga cikinsu hadda jariri.
A ranar shida ga watan Afrilun da ya shude ma dai, jiragen yakin kawancen a Saudiyya sun kai kwatankwacin wannan harin,a garin Jar da ke gundumar Abas wanda ya shafi fararen hula.
Tun a shekarar dubu das ha biyar ne dai Saudiyya ta shelanta yaki akan kasar Yemen, wanda ya zuwa yanzu ya ci dubban rayuka da kuma jikkata wasu dubun dubata. Bugu da kari,wasu dubun dubatar mutanen kasar sun zama ‘yan gudun hijira saboda rusa matsugunansu.
Har ila yau, hare-haren na Saudiyya sun yi sanadiyyar lalata asibitoci da kuma cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar ta Yemen.