Jaridar Quds Arabi ta bayar da rahoton cewa, a cikin wani bayani da ya fitar, kwamitin malaman musulmi na duniya ya gargadi gwamnatin kasar Faransa kan yin shigar shugula a cikin harkokin musulmi na kasar.
Ya ce abin da gwamnatin Faransa take shirin yin a takaita harkokin musulmi da lamurransu na addini a kasar yana a matsayin take hakkokinsu na addini, wanda babu wata doka ta duniya ta amince da hakan.
Daghi ya ce suna kiran gwamnatin Faransa da ta gaggauata dawowa daga rakiyar tunanin da take yi na cewa za ta sanya musulmi su yi addininsu daidai da maharta, ba mahangar da addinin muslunci ya koyar da su ba.