IQNA

Malaman Kiristoci Sun Halarci Taron Bude Wani Masallaci A Kasar Masar

20:14 - November 27, 2021
Lambar Labari: 3486613
Tehran (IQNA) Jami'ai a lardin Qana na Masar sun ce halartar kiristoci a wajen bude wani masallaci a garin Farshat, wata shaida ce ta kiyaye hadin kan kasa da kasancewar 'yan uwantaka da abokantaka a tsakanin mabiya addinai daban-daban a kasar.
Shafin jaridar Akhbar Yau ya bayar da rahoton cewa, a birnin Farshout da ke lardin Qana da ke kudancin Masar, an ga wani kyakkyawan yanayi na yadda al'ummar kiristoci suka halarci bikin bude sabon masallacin Al-Rahman a wannan birni tare da tare da sauran musulmi.
 
Taron kaddamar da bikin bude wannan masallaci da aka gina da kudin jama'ar Farshut, ya samu halartar Sheikh Yasser al-Arshi shugaban ofishin bayar da tallafi na Farshut, da kungiyar malaman Azhar da na addinin Islama da na Kirista da kuma jami'ai da mutanen gari.
 
Daga malaman kirista da suka halarci taron akwai Zakariyya da Benood, shugaban cocin Deir Bahjar Al-Dahsa da Al-Malak, Kirista da Musulmi suna zumunci a Masar, wanda yake a  matsayin darasi abin koyi ga al'ummomin duniya.
 

4016444

 

captcha