A cewar jaridar Correct Nigeria, wannan kungiya ta musulmi karkashin jagorancin Muhammed Muritala Chukwuemeka, daya daga cikin shehunan yankin, sun shafe shekaru biyar suna fassara.
"An kwashe kusan shekaru biyar ana kammala wannan fassarar," in ji Chukomka. Muna rokon ’yan Najeriya masu kishin kasa da masu hannu da shuni da su taimaka mana wajen yada labarai.
A halin yanzu, an buga kwafi 500 na wannan fassarar kuma an aika kwafi 100 zuwa kudu maso gabashin Najeriya.
Ya ce manufar kungiyar ita ce isar da sakon Allah ga ‘yan uwanta ‘yan kabilar Igbo ta hanyar Alkur’ani da aka fassara.
A gobe Juma’a 1 ga watan Yuli ne za a gabatar da tarjamar a masallacin Ansarul Din da ke Abuja, bayan sallar Juma’a.
Kabilar Igbo dai ƙabila ce ta ƴan asalin yankin kudu ta tsakiya da kuma kudu maso gabashin Najeriya mai kimanin mutane miliyan 33 a Najeriya. Kimanin karin miliyan daya na wannan kabila suna zaune a wasu kasashen Afirka.