Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Masri Al-Youm cewa, an ji girgizar kasar a daren jiya a Palastinu a garuruwan Ramallah, Al-Bireh, Nablus da Quds da aka mamaye.
A cikin wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta, ma'aikatan gidan rediyon Nablus sun shaida wata girgizar kasa da ta girgiza fitulun da ke rataye a rufin ginin.
Jalal Debik, darektan cibiyar nazarin girgizar kasa ta jami'ar kasar An-Najah ta Nablus, ya sanar da cewa: Girgizar kasar ta afku a nisan kilomita 13 daga arewacin birnin Nablus, mai girman 3.7 zuwa 4 a ma'aunin Richter da zurfin kilomita 10. .
Gidan rediyon kur'ani mai tsarki daga Nablus gidan rediyo ne mai zaman kansa kuma na musamman a fannin kur'ani mai tsarki da iliminsa wanda ya fara watsa shirye-shiryensa a shekara ta 1998 (1419H) daga birnin Nablus na kasar Falasdinu. Manufar rediyo ita ce karfafa alakar mutane da kur’ani mai girma, fahimtar da sanin hukunce-hukuncen sa.