Ranar 15 ga watan Sha’aban, ko kuma Nisfu Sha’aban, wadda ke cika maulidin Imam Zaman (AS), ta zo ne a ranar Laraba 8 ga watan Maris na wannan shekara.
A kowace shekara miliyoyin mabiya mazhabar shi'a a duniya suna gudanar da bukukuwan girmama wannan rana.
A wannan gagarumin biki, masallacin Jamkaran yana samu halartar dubban daruruwan maziyarta.