Bangaren siyasa, jagoran juyin juya halin muslunci ya aike da wani sako zuwa ga shugaban kasa da sauran jami'an kasa kan muhimamncin zama cikin fadaka dangane da batun yarjejeniyar nukiliya da kuma yadda za a fskanci daya bangaren.
2015 Oct 21 , 23:04
Bangaren siyasa, Jagoran juyin Islama ya yi kakakusar suka dangane da yadda kasashen yammacin turai suka yi gum da bakunansu kana bin da ya faru a Mina, musamman ma masu da’awar kare hakkin bil adama, inda ba za a manta da wannan lamari ba, kuma aikin jami’an diplomasiyya da na ma’aikatar hajji ne su bi kadun wannan batu.
2015 Oct 20 , 23:13
Bangaren siyasa, Jagoran juyin juya halin muslunci ya jaddada wa jami’an gwamnati cewa, ci gaba n da Iran ta samu a dkkanin bangarori na nukiliya da sauran gaskiya ne, kuma dakushe zukatan matasa kan kara himma babban cin amana ne ga kasa.
2015 Oct 14 , 22:41
Bangaren siyasa, a ganawar da jagoran juyin juya halin muslunci na Iran ya yi tare da shugaban hukumar radiyo da talabijin ta kasar da kuma manyan daraktoci na hukumar ya bayyana cewa dole a zama cikin fadaka domin makiya suna yin amfani da hanyoyin sadarwa wajen hankoron juya manufar juyin Islama.
2015 Oct 13 , 21:23
Bangare siyasa, Ayatollah Sayyid Ali Khameni a lokacin da yake ganawa da manyan kwamandojin rundunar kare juyin juya halin muslunci na ruwa da kuma ma’aikata a wannan bangare na kudancinkasar ya ce, umarnin kur’ani na saka tsoro a zukatan makiya ya tabbata a kudancin kasar.
2015 Oct 07 , 20:42
Bangaren siyasa, an gudanar da zaman makoki na mahajjatan da suka rasa rayukansu sakamakon abin da ya faru a Mina a wajen aikin hajjin wannan shwekara tare da halartar Ayatollah Sayyid Ali Khamenei a Husainiyyar Imam Khomenei (RA)
2015 Oct 04 , 22:49
Bangaren siyasa, Ayatollah Mowahadi Kermani wanda ya jagoramnci sallar Juma’a ya bayyana cewa dole ne abin da jagora ya fada ya zama a cikin kunnuwan wadanda suka haddasa mutuwar alhazai na kasashen msuulmi kuma dole ne a canja salon tafiyar da aikin hajji.
2015 Oct 02 , 23:29
Bangaren siyasa, jagoran juyin juya halin muslunci ta Iran ya bayyana cewa, nuna rashin mutunci da rashin sanin ya kamata ga mahajjatan Iraniyawa zai fuskanci martini, idan kuma aka tashi mayar da martanin zai zama mai mni matuka a kan wadanda suka aikata hakan.
2015 Oct 01 , 22:41
Bangaren siyasa, Dr Hassan rauhani ya bayyana gwamnatin Saudiyya da cewa it ace take da alhakin dukkanin abin da ya faru kuma dole ne su amince da cewa laifinsu, domin kokarin dora wa wasu alhakin hakan shi ne babban abin da ke kara tabbatar da rashin gaskiyarta a cikin wannan lamari na kisan mahajjata.
2015 Oct 01 , 22:37
Bangaren siyasa; Jagoran juyin juya halin Musulunci a lokacin da yake gabatar da darasinsa na "Bahasul Kharij" yayi karin haske dangane da turmutsitsin da ya faru a Mina da yayi sanadiyyar mutuwa da raunata wani adadi mai yawan gaske na mahajjatan da suka fito daga kasashe daban-daban na duniya.
2015 Sep 27 , 23:50
Bangare siyasa, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa an kafa wani kwamiti domin bin kadun alhazan kasar Iran da suka rasu a hadarin Minna a yau.
2015 Sep 24 , 23:38
Bangaren siyasa, Ayatollah Ozma Sayyid Ali Khameni jagoran juyin juya halin muslunci ya fadi a cikin sakonsa ga mahajjatan bana cewa, babbar damuwar musulmi a halin yanzu ita ce bakar siyasar Amurka da munanan laifukan sahyuniyawa da keta alfarmar masallacin Aqsa.
2015 Sep 23 , 20:52