Bayanin ya ce baya ga tarjama jawabin an kuma saka shi a cikin shafukan yanar gizo gami da jaridu da kafofin yada labarai da daman a kasashen ketare.
Daga cikin kasashen kuwa akwai:
Aljeriya: jaridun Alkhabar, Alshuruq, Akhbar yaum da kuma Alwatan.
Ethiopia: jaridar turanci ta Daily Monitor.
Tunisia: an saka tarjamar jawabin a jaridun Sahwa, da Al-sabah.
Australia: Jaridar mako-mako mai suna Iran.
Turkiya Ankara: a cikin jaridar Aidinlik, sai kuma tashar talabijin ta 14 ta Turkiya.
India: an yada jawabin a tashar WIN da kuma jaridar Sahafat.
Pakistan Kuita: wanna labara ya zoa cikin jaridun Azadi, da Balochestan da kuma Express.
Armenia: a kasar kuma an yada wannan labari a cikin wasu kafofin yada labarai na gidajen talabijin da kuma jaridu na kasar, sai kuma laccoci da aka gudanar a jami’oi wanda masana da suka yi ta gabatarwa da nufin kara sanar da mutane halin da ake ciki.