Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, wasu majiyoyi masu tushe daga fagen daga a kasar Syria sun tabbatar
da cewa, Sa'ad Al-husaini dan kasar Saudiyyah, wanda aka fi sani da Abu
Sa'ad, daya daga cikin manyan jagororin kungiyar ISIS, yana daga cikin
manyan kwamandojin kungiyar 'yan ta'addan na ISIS da suka halaka a daren
jiya, bayan saukar makaman ballistic da dakarun IRGC suka harba daga
cikin kasar Iran zuwa kan sansaninsu da ke Deir Zur a cikin kasarSyria.
Dakarun na IRGC sun ce wannan somin tabi ne na alwashin da suka sha
na mayar da martani da daukar fansa a kan harin da kungiyar ISIS ta kai a
Tehran, kuma akwai wasu matakan na gaba da suke tafe a kan kungiyar ta
ISIS da masu daukar nauyinsu.
Harin na Iran dai ya girgiza dukkanin wadanda suke da hannu a hare-haren da yan ta'addan suka kai a birnin Tehran a kwanakin baya.
3611235