Cibiyar koyar da Alkur’ani ta Iqna bayan nakalto daga majiyar Ma’a ta watsa labarin cewa: sojin gwamnatin Haramtacciyar kasar Isra’ila sun kai mamaye da makamai kan cibiyar koyar da alkur’ani ta Zaid bin Sabit a garin Kudus tare da yin awangaba da duk wani abu da ke cibiyar.
Har ila yau sojin Isra’ila sun bude wuta kan mutanan yankin domin hana su kusantar cibiyar da hana yan gwagwarmaya isa gurin.Bugu da kari sojin gwamnatin Haramtacciyar kasar ta Isra’ila sun tsare Sufiyan Jadullah shugaban cibiyar ta Zaid bin Sabit tare da wulakanta takardun Alkur’ani a cibiyar.
359271