Bangaren kasa da kasa: Musulmin kasar Rasha daga yankin (Nijni Novgorod) sun bukaci sauran musulmin kasar da su kaurace wa sayen kayayyakin Holand, sakamakon shirya fim din cin zarafi ga manzon Allah (SAW) da aka shirya a kasar.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran kasar Faransa AFP cewa; daya daga cikin jagorin musulmin kasar Rasha Abdulbari Moslimov ya bayyana cewa, mafi yawan msulmin Rasha musamman a yankin Nijni Novgorod suna sayen furanni ne da ake zowa da su daga kasar Holand, amma sanadiyar shirya wani fim da aka yin a ci zarafin manzon Allah (SAW) a kasar, suna kiran dukkanin musulmi da su kaurace wa sayen furannin na Holand, domin kare matsayin manzon Allah tsirar Allah da amincinsa su tabbata gare shi da iyalan gidansa.
369932