IQNA

Cibiyoyin Ilimi Na Biranan Najaf Da Qom Suna Raya Ilmomin Kur'ani

14:55 - August 02, 2009
Lambar Labari: 1808707
Bangaren kasa da kasa; Cibiyoyin ilimi na biranan Qom da Najaf suna taka gagarumar rawa wajen yada ilmomin kur'ani mai tsarki ta hanyoyi da dama.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga bangaren yada labarai na cibiyar yada al'adu da danganataka tsakanin kasashen musulmi ta kasar Iran cewa; Cibiyoyin ilimi na biranan Qom da Najaf suna taka gagarumar rawa wajen yada ilmomin kur'ani mai tsarki ta hanyoyi da dama, duk da cewa suna yada ilmomin na hukunce-hukuncen addini dad a hadisi da usul gami da ilmin akida wato tauhi da dai sauransu, amma gishikin dukkanin wadannan ilmomi da cibiyoyin suke bayarwa ya ginu ne a kan kur'ani mai tsarki. Bayanin ya ci gaba da cewa wadannan manyan cibiyoyi biyu ba za a taba mayar da su gefe ba, domin kuwa su ne gishikin dukkanin ilmomin mazhabar iyalan gidan manzo a wannan zamani.

441564

captcha