IQNA

A Birnin Nairobi Iraniyawa Za Su Gudanar Da Baje Kolin Kur'ani

16:43 - September 12, 2009
Lambar Labari: 1825185
Bangaren kasa da kasa: bayan da aka samu halartar mutane masu yawan gaske da suka halarci kasuwar baje kolin kur'ani a birnin Munbasa na kasar Keniya za a gudanar da irin wannan kasuwar baje koli a birnin Nairobi fadar mulkin wannan kasa ta Keniya.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce daga kasar ta Keniya ta watsa rahoton cewa; wannan kasuwar beje kolin ta hada abubuwan rubuce-rubuce na zane-zane na Muhammad Muwahidiyan Attar da na Mahdi Muwahidiyan kuma za a kwashe kwanaki uku a gidan ajiyar kayan tarihi ana gudanar da wannan kasuwar baje kolin.Kuma wannan yana tabbatawa da nuni da yadda tarihin Musulunci da musulmi yake cike abubuwan tarihi.

463345

captcha