Bangaren kasa da kasa; A lokacin da yake gabatar da jawabin bude taron hadin gwiwa tsakanin gwamnatin Rasha da duniyar musulmi, Alexender Torshen ya bayyana cewa musulmin Rasha su ne igiyar daura kyakkyawar dangantaka tsakanin Rasha da sauran kasashen musulmi.
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin internet na kamfanin dillancin labaran Rusia alyaum cewa; A lokacin da yake gabatar da jawabin bude taron hadin gwiwa tsakanin gwamnatin Rasha da duniyar musulmi, Alexender Torshen ya bayyana cewa musulmin Rasha su ne igiyar daura kyakkyawar dangantaka tsakanin Rasha da sauran kasashen musulmi. Bayanin ya ci gaba da cewa An bude zaman taron ne da karanta bayanin shugaban kasar rasha Dmitry Medvedev, sai kuma bayanin babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi Ihsan Oglo. Bayanin ya ksrs da cewa babbar manuufar gudanar da wannan zaman taro ita ce kara kusanto da fahimta tsakanin bangarorin biyu, ta yadda za su ci gaba da gudanar da aiki kafada da kafada domin amfanar juna. 469323